advanced Search
Dubawa
7402
Ranar Isar da Sako: 2012/07/23
Takaitacciyar Tambaya
Shin abin da ake fada game da kafy cewa ya kunshin kadan daga hadisai ingantattu da ababan yarda gaskene kuwa?
SWALI
Ana cewa kulainy mai littafin kafy (RA) ya ce kadan ne ingantattun hadisai, hadisai ingantattu cikinsa kadan ne, shaidai kan hakan shi ne litattafan da aka yi bayan kulainy, inda waheed bahbaha’iy (RA) yake cewa ‘an samu hadisai da yawa cikin kafy wadanda ba su dangane zuwa ga ma’asumi ba shin wannan magana gaske ce?
Amsa a Dunkule

Ma’aunai da magwajai da kulainy ya kawo basuyi daidai da hadisin ba sai dai ta kebantane da hadisan da ya samo har ma da aka tauye kawai, bawai yana nufin wannan awon ya hau kan kowane hadisi ba domin sanin hadisi ingantacce ta hanyar bangarori uku da aka musalta cikin Kur’ani mai girma,sabawar dukka da zabi, kai ayon ma yafi haka girma, domin rubuta litattafanda suka dace ba ya nufin rashin ingancin na farko, saboda haka rubuta littafi ga marubucin daya dace da wani dalili ne na duba kebantacce da ya sha banban da suran shi kansa bukatar rubuta sabon littafi, wannan shi ne abin da fadhul kashany ya yi nuni da shi cikin mukaddimar littafinsa alwafy, i’itirafin su kansu malaman litattafai ukun wadanda suka dace da kafy a nan kuma yai ikirarin muhimmancinsa.

Amsa Dalla-dalla

Domin warware amsar babu makawa saimunyi nuni zuwa wasu alamu da zasu zame mana hanya,

  1. ana sanya kulainy (RA) daga cikin manyan malaman Shi’a lokacin karamar gaiba wannan daga kadarinsa ya kara girma a wajan da yawa daga malamai,[1] allama Muhammad attaky (majlisy) yana cewa tabbas a tsakiyar Shi’a ba a samu misalinsa ba,duk wanda ya yi aiki da ruwayar daya ciro,da rubutun littafi zai samu cewa wannan wani irin mutum ne da allah ya tanadar.[2]
  2. Ma’aunai da magwajai da kulainy ya kawo basuyi daidai da hadisin ba sai dai ta kebantane da hadisan da ya samo har ma da aka tauye kawai, bawai yana nufin wannan awon ya hau kan kowane hadisi ba domin sanin hadisi ingantacce ta hanyar bangarori uku da aka musalta cikin Kur’ani mai girma, sabawar dukka da zabi, kan ayon ma yafi haka girma, wannan shi ne abin da muka samu cikin fakarori masu zuwa.
  3. sananne ne cewa malaman karshe da suke a lokutan malaman kutubul arba a wanda kulainy na cikinsu suna da hanya da ma’auna na musamman wajan tabbatar da ingancin ruwaya da ta tsaya kan tushen sigar mai ruwaya, mannan shi ne abin lura ta wajan magaba ta inda suke tabbatar ingancin hadisi wanda yake da siga a tare da shi.[3] sai magana dangane da matanin hadisi suka zamo sharadinsu shi ne kawai danganewarsa zuwaga ma’asumi (a.s).
  4. hakika mun warware wani abu daga ruwayoyin kafy muka kyale wasu, sai dai akwai wanda yai duba zuwa gareta duba na musamman da yake la’akari da ita. Sheikhul muffed ya tafi kan cewa shi kafy yafi kowane littafin Shi’a fifiko da amfani.[4] sayyid murtadha kuma ya ce: babu mamaki mafiya yawa daga litattafan kutubul arba a ana ganinsane daga tushe daya (ahad), sai dai za a iya samun yankewarta daga ayimma (a.s) kamar;

(a)- ta hannun yan Shi’a da yawan yaduwa,

(b)- karnoni masu nuna ingancin ruwayoyi.[5]

kai duk da masu hakikancewa kama karky dan Muhammadul amin istrabady cewa ba a yi wani littafi misalinsa a wajan Shi’a ba.[6] najashy ya jefeshi cewar kulainy littafin ma’abotanmu ne a lokacinsa da ra’a yi kuma shi ne mafi fuskarmu kuma mafiya shakuwarmu mutane a hadisi da tabbatar da hadisi, ya rubuta littafi mai girma da aka sani da kafy cikin shekara ishirin (20).[7] amma dan uwa ma’abocin usul ya ce: hakikaa hadisan da ke kutubal arba a da misalinsu sun wuce karnoni, kuma an cirota daga litattafan usul da litattafan da suka hada da ita ba tare da canjawa ba.[8] ya kuma kara cikin maganar karbuwa da cewa: alamunn karbuwar ta bangaren aiki ya bayyana ta yadda bai rataya da ilimin rayuwa da wasunsu ba kamar litattafain da aka fada mana hudu ba (kutubul arba a) domin ita an rawaiceta ne baki daya da ilimi mai inganci wanda yake da yawa tare da falala da aka amfanu da ita tsawon karnonin da suka shude, kuma ba a cika shiga don ijaza ba a mafiya yawan lokuta.[9] ina nufin karnonin sun samu dalili wajan nuna ingancin kutubul arba a da ta wadatu daga gyararraki, faidhul kashany (RH) ya tafi kan littafin kafy shi ne mafi cikar litattafai kuma mafi daukakarsu ya taro abubuwa da yawa na rassa da tussan ibada kuma ya kubuta daga aibobi kuma yana tare da falaloli,[10] sayyid khu’iy ya kawo cikin mukaddimarsa cewa yaji malaminsa sheikh Muhammad Husain anna’iny (KS) a wajan bahasinsa yana cewa munakasoshi cikin danganen ruwayoyin kafy sun wuce yadda ake zato,[11] muna iya waiwayawa ga nazariyyar inganci a wannan fage ita ce maganar tsakiya ko ta dalili wadda ta tsaya tsakanin daidaiku da bangarori, da wadda ta tafi kan cewa alkafy a lokacin da ya hado ingantattun ruwayoyi a cikinsa da muhimmanci da yawa hakanan ya hada da ruwayoyi raunana.

  1. domin rubuta litattafanda suka dace, ba ya nufin rashin ingancin na farko, saboda haka rubuta littafi ga marubucin da ya dace da wani dalili ne na duba kebantacce da ya sha banban da suran shi kansa bukatar rubuta sabon littafi, wannan shi ne abin da fadhul kashany ya yi nuni da shi cikin mukaddimar littafinsa alwafy, inda yake cewa: da ina nan, wannan sha’ani tare da karancin buktu wadda tazo ne lokacin hadari wajan sanya wannan aiki, sai dai cewa zamani bawai yana bayyana yadda mazaje suka yi bacci ba ne, bai tattauna hukunce hukuncen Abul Hassan ba wannan aikin jama’ane da yan uwa da suka fuskanto zuwa fuskokin zuciyarsa masu tsarki, wannan ya sani sanyin jiki ta wani bangaren a cikin wannan huduba mai girma da riko da dukkanin wannan ta yin ta’alifi da riko da gini kan wadannan ma’anonin da suka yi daidai da iyakarta, wanda cikinta ya sharanta ta a cikinta da yardar allah, ya hadashi hadawa kuma ya habakashi ya ilimantar da shi ilimantarwa ya tsarashi tsarawa kuma ya saukake hanyar da za a fahimceshi, na bada kokarina kan ka da wani hadisi ya ware masa ko sanadi da zai hada duk litattafai hudun daidai yadda zan iya kuma nayi sharhin wasu daga cikinsu kuma na daga wasu abubuwan da babu mamaki suna bukatar bayani da sharhi takaitacce ba mai tsayi ba.[12] har ma da i’itirafin su kansu malaman litattfai ukun wadanda suka dace da kafy a nan kuma yai ikirarin muhimmancinsa.
  2. Takaitacciyar maganar (nazariyyar) waheed bahbaha’iy cewa da yawa daga marawaitan kafy ba su dangakne da ma’asumai ba sai dai suna danganewa ga dayan sahabbansu.[13] don haka abin da ake danganta musu baya inganta cikin ainihin tambayar da ake cewa “an an samu hadisai da yawa cikin kafy wadanda ba su dangane zuwa ga ma’asumi ba” babu mamaki wannan istimbadi (tsamo hukunci) da tacewa daga maganar da muka fada mun sani cewa rashin danganewar ruwaya zuwa ga ma’asumi ba ya lazimta kasancewar ruwayar karya ko kuma rarrauna, wannan kuwa shi ne idan manya irin su Ali dan Ibrahim da ayyub[14] suna ganin daga ma’asumai yake, daganan ne marigayi kulainy ya yi riko da nakaltowa daga wajansa abin da ya dangane dasu ba wai sai ya dangane zuwa ma’asumi ba.

 


[1] Kulainy mai littafin kafy babba, intisharatu amir kabir, tahran page 247, 1363

[2] Usulul kafy, fassarar sayyid jawad musdafawy, intisharatul wafa’a, mukaddimar mai gabatarwa, page 8

[3] Aliyyu akbar, mikyasud diraya fi ilmur ruwaya, page 44.

[4] A’alamul hidayatur rafee’ah fi i’itibari kutubul arba ah almaneeah, Aliyyu namazy shahrudy page 133,

[5] Wasa’ilush Shi’a, sheikh hurril amily, bolume 2 page 76; muntakal jimal fi ahadisis sihsu wal hisan bolume 1 page 8

[6] Subhany, kulliyyat fi ilmur rijal page 360;

[7] A’alamul hidaya, page133; wanada aka ciro daga rijalun Najashy, ka duba tarjamar a Mu’ujamu rijalul hadith na sayyed khu’iy.

[8] Mu’alimul usul, Hassan dan zainuddeen page 185.

[9] A’alamul hidayatur rafee’ah fi i’itibari kutubul arba ah almaneeah, Aliyyu namazy shahrudy wanda aka ciro daga mu’alimul usul fi mabhathul akhbaar page 152.

[10] Usulul kafy, mukaddimar mai tarjama, page 9.

[11] Mu’ujamu rijalul hadith na sayyed khu’iy. Page 99.

[12] Alwafy, fadhul kashany, maktabatul islamitta page 7,

[13] An cirota ne a matsayin misali daga littafin Diyyat daga wasu ruwayoyin da suka kare zuwa Aliyyu dan Ibrahim da abi ayyub ba zuwa ga ma’asumai ba (duba rasa’ilul usuliyya na Waheed bahbaha’iy page 7-8);

[14] Mustadhrafatul ma’any, Aliyyu namazy shahrudy, page 93 da 213 bugun farko 1422;

 

TARJAMA YA JAWABU KATIKA LUGHA NYENGINE
Mahanga
Idadi ya maoni 0
Tafadhali ingiza thamani
Imel : Yourname@YourDomane.ext
Tafadhali ingiza thamani
Tafadhali ingiza thamani

Tambayoyi Masu Fadowa

Mafi Dubawa