advanced Search
Dubawa
9081
Ranar Isar da Sako: 2011/01/18
Takaitacciyar Tambaya
Shin zai iya yuwuwa a kai ga martabar ubangijintaka?
SWALI
Shin zai iya yuwuwa a kai ga martabar ubangijintaka?
Amsa a Dunkule

Makamin matsayin ubangijintaka yana da matakai da marhaloli mabambanta, kuma don a samu wannan amsar dole ne a ga dukkan martabobi da ma’anonin baki daya. Idan abin da ake nufi da kai wa matakin ubangijintaka shi ne zatin mutum ta canja da sauyawar abin halitta ya koma mahalicci to wannan al’amari a fili yake cewa batacce ne kuma ba zai yiwu ba. Sai dai wannan maganar zata iya yiwuwa tana nuni da wata ruwaya ce da aka karbo daga imam Ja'afar Sadik (a.s) wacce yake fada cikinta cewa; “ibada jauhari ce, badininta ubangijintaka ce” ma’anar wannan maganar shi ne isuwa zuwa ga matukar bauta da narkewa cikin zatin Allah, ba ana nufin mutum ya koma ubangiji ba.

Amsa Dalla-dalla

Makamin matsayin ubangijintaka yana da matakai da marhaloli mabambanta, kuma don a samu wannan amsar dole ne a ga dukkan martabobi da ma’anonin baki daya. Idan abin da ake nufi da kai wa matakin ubangijintaka shi ne zatin mutum ta canja da sauyawar abin halitta ya koma mahalicci to wannan al’amari a fili yake cewa batacce ne ba zai yiwu ba, kuma saken zuci ne kawai da ba shi da wani tushe, kamar yadda ya zo a kur’ani mai girma cewa Fir’auna  ya yi da’awar ubangijintaka sai ya kama hanyar tabewa kamar yadda yake a fadinsa madaukaki: Sai ya ce ni ne ubangijinku mafi daukaka, sai Allah ya rike shi da azabar karshe (lahira) da ta farko[1] (duniya).

Sai dai abin da ake kawowa a bahasin irfani a babin tajallin siffofin Allah da makamancinsa wannan wata maganar ce daban da ta saba da waccan, kuma tana da alaka da ruwayar da aka karbo daga imam Sadik (a.s) cewa: “ibada jauhari ce, badininta ubangijintaka ce[2]” kuma shigen irin wannan maganar ta zo a kalaman masu irfani da suka yi bayanin sa dalla-dalla.

Wannan maganar a cikinta akwai nuni da mafi daukakar matsayi da martabobi da mutum yake kaiwa zuwa gare su, bayan ya narke cikin zatin Allah sai kuma ya wanzu ciki da wanzuwar Allah, kuma matsayin wanzuwa bayan narkewa ba yana nufin mutum zai canja ya koma zuwa Allah ubangiji ba, ko kuma ya kai ga matsayin ubangijintaka, sai dai abin da ake nufi da narkewa da sabewa (yin saba da fita) daga zatinsa shi ne mutum zai zama mahallin tajallin (bayyanar) siffofin Allah ne.

Saboda haka ba yadda mutum zai iya kaiwa zuwa ga matsayin ubangijintaka ta kowane hali, sai dai yana iya narkar da zatinsa sai ya bayyana da siffofin ubangiji da yake bayyanar da su ga wannan mutum da ya narke, kamar dai yadda arifai suke cewa “matukar samuwa ta wanzu (to shi ma zai wanzu)” ba zai yiwu ubangiji ya zama cikin bawa ba, da nufin cewa bawa yana nan dai bawa, ubanigiji kuma yana dai ubangiji, ba zai yiwu a hada su biyu ba.

Kuma an yi nuni da wannan matsayi a wasu ruwayoyin daga cikin akwai hadisin nan na kudsi shahararre da yake cewa: “Bawa ba ya gushewa yana kusanta zuwa gare hni da nafiloli da ibadoji har sai na so shi, idan na so shi sai in zama jin sa da yake ji da shi, da ganin sa da yake gani da shi, da hannunsa da yake riko da shi, da kafarsa da yake tafiya da ita” [3].

Kamar yadda komawa da karanta ruwayoyin da ziyarorin da kuma kalaman da suke zuwa daga ma’asumai da matsayinsu yana nuna mana wannan matsayi mai girma, sai dai ta wata fuskar kuma akwai wasu mutane masu gazawa ga fahimtar irin wannan kalamin wadanda suke ganin sa shisshigi ne a addini, sai dai mu zamu yi bayanin wannan ruwayar wani lokacin.

Daga irin wannan akwai maganar wasu arifai da ta zo don bayanin matakai da matsayoyi cikin bayani na falsafa da hikima, daga cikinsu akwai Mulla Sadra a littafinsa “Ikazun na’imin” (farkar da masu bacci) da ya yi bayanin tafiyar masu irfani zuwa ga Allah madaukaki, yayin da ya kai ga matsayin tauhidi sai yake cewa:

“An ce wannan tauhidin shi ne suturta fuskar bauta da fuskar ubangijintaka, da boye falakin zatinsa yayin samun ranar girma da daukaka, sai ubangiji ya kasance a zahiri bawa kuwa ya kasance a boye…, kuma zai iya yiwuwa a samu canja siffar mutum da siffar Allah ban da zati, don haka duk sa’adda wata siffa (ta bawa) ta dauke ta gushe sai wata siffar (ubangijintaka) ta maye gurbinta, sai gaskiya (ubangiji) ya kasance jinsa, da ganinsa, kamar dai yadda hadisi mashhuri ya yi bayani, sai mutum ya yi tasarrufi a cikin halittu da abin da Allah ya so” [4].

Haka nan ne Mulla Ali ya rubuta a game da wannan lamarin yana mai cewa:

A lokacin ne sai bawa ya zama kamar fainsa (s.a.w) cewa: Allah ya halicci Adam (a.s) a bisa surarsa, kuma matsayin surar abu shi ne matsayin fuska da inuwa daga hakikanin zatin abu da ma’abocin fuska da inuwa, kamar dai yadda imam Sadik (a.s) ya ce: Bauta Jauhari ce, badininta shi ne ubangijintaka. Da wannan ne ya yi nuni da matsayinsa a halarar ubangiji  yayin da ya ce: duk wanda ya gan ni to ya ga hakku (ubangiji), kuma imam Sadik (a.s) yana fada game da fadin Allah madukaki: duk wani abu mai halaka ne sai fuskarsa. Cewa; mu ne fuskar. Da wannan ne zamu ga alkiblar masu irfani sarkin muminai imam Ali (a.s) yana cewa: sani na da haske, shi ne sanin Allah. Domin matsayin haskensa (a.s) daga halarar zatin Allah yake, wanda yake zati ne na hasken haskaka mai rinjaye kan komai, kuma shi ne matsayin surar abu kuma fuskarsa[5].

Hakika ma’abota irfani sun yi magana a baitocinsu da kalamansu game da wannan lamari, daga cikinsu akwai sayyid haidar amuli yayin da ya rubuta musamman game da matsayin wilaya ta musamman a irfani yana mai cewa: wilaya ta musamman ita ce narkewar bawa a cikin gaskiya, waliyyi shi ne wanda ya narke a cikin hakku (ubangiji) kuma ya wanzu da shi.

Ba ana nufin narkewa ita ce rasa bawa baki daya ba, sai dai abin da ake nufi da wannan shi ne fuskacin da yake bawa zata narke cikin fuskancin ubangijintaka, domin kowane bawa yana da fuskacinsa a halarar ubangiji da ita ce aka yi nuni da ita a fadinsa maduakaki “Kowa yana da fuskacinsa da yake jibintarta”, aya. Wannan kuwa ba ya samuwa sai dai cikakken fuskanta zuwa ga janibin fuskacin ubangiji sake babu wani kaidi da sharadi, don da wannan ne fuskancin hakirkarsa ta ubangijintaka zan ta karfafa sai ta yi rinjaye kan fuskacin halittarsa har sai ta rinjaye ta, ta narkar da ita baki daya, kamar dai wata kwayar gawayi ce da aka sanya ta cikin wuta.

A bisa haka ne mutum kamili ya kasance shi ne mai alamta siffofin Allah baki daya, kuma idan mutum ya kai kololuwar kamalar karshe to zai iya kasancewa halifan siffofin Allah a duniya, domin siffofin Allah suna bayyana ga mutum a martabar narkewa. Wannan kuwa ba yana nufin magana ne kan ubangijintakar mutum ba, wannan yana nuna bayyanar alamtuwar Allah ne a mutum, wannan kuwa ba yana nufin sun hade da Allah ba, ko kuma mutum ya canja ya koma ya sauya zuwa ga Allah ba, kamar yadda muka yi nuni da haka a baya.

 


[1] Annazi’at: 24, da 25.

[2] Misbahus shari’a, s 7, mu’assasar al’a’alami lil matbu’at, 1400 k.

[3] Awalil la’Ali, j 4, s 103, manshurati sayyidus shuhada, kum, 1405 k.

[4] Mulla Sadra, Ikazun na’imin, s 58, anjamane hikmat wa falsafeye iran.

[5] Nuri, almaula Ali, ta’alikat alal mafatihul gaib, s 742, muassasar tahkikate farhangi.

 

TARJAMA YA JAWABU KATIKA LUGHA NYENGINE
Mahanga
Idadi ya maoni 0
Tafadhali ingiza thamani
Imel : Yourname@YourDomane.ext
Tafadhali ingiza thamani
Tafadhali ingiza thamani

MPANGILIO WA KIMAUDHUI

Tambayoyi Masu Fadowa

  • menene abin sha mai tsarkakewa?
    18306 شراب طهور 2012/09/16
    "Ashsharab" abin nufi duk abin sha "Addahiru" abin nufi mai tsaki mai tsarkakewa wannan kalma an yi amfani da ita a cikin ayoyi daban-daban a gidan aljanna ana samun abin sha mai tsarki mai dadi iri-iri mai yanayi kala-kala, hakika Kur'ani mai girma ya kawo maganar sa ...
  • Mece ce Daraja, Mene ne hanyoyinta?
    14854 Halayen Nazari 2012/07/24
    Karimci; yana nufin nisantar abubuwan wulaknata kai da tsarkaka daga dukkan mummunan hali, amma karimi siffa ce da ake gaya wa mutum mai daraja da ya tsarkaka daga dukkan wulakanta kai da munanan halaye. Kuma ana amfani da karama a matsayin kalma da take kishiyantar ...
  • Ida mutum ya yi wa mace wakilci a auren mutu’a amma bai gaya mata yawan sadakin da mudda (tsawon lokaci) ba, shin auren ya inganta kuwa?
    11492 متعه 2012/07/25
    Akwai amsoshi daban-daban tsakanin fatawoyin malamai kamar; AYATULLAHI KHAMNA’IY (MZ); Idan ta wakilta shi a kan komai hatta a sadaki da mudda babu matsala mutukar an cika sauran sharudda kamar izinin uba, kaka, ko wa, ga yarinya budurwa, don cika ...
  • Shin Mace zata iya yin Limancin sallar jam’i ga mata irinta?
    11159 شرایط امام 2012/11/04
    An samu sabanin ra’ayoyi tsakanin malamai maraji’ai game da limancin mace ga mata a sallar jam’I da zamu kawo bayanin kamar haka: 1. Mafi yawan marja’ai sun tafi a kan cewa bisa ihtiyadi wajibi ne limancin mace ga ‘yan’uwanta mata ba ya inganta
  • Me ake nufi da Ci gaban al’umma a cikin siyasar musulunci?
    12047 کلیات 2012/07/24
    Cigaba da wayewar al’umma yana daga cikin isdilahohin da suka yadu a cikin tunanin yammacin duniya da malam palsafar siyasar yammacin duniya da aka yi masa fassarori mabambanta daga cikin bayanai da aka yi wa wannan isdilahin, da muna iya gane cewa mahangar da ake da ita ...
  • Me ye gwargwadon ikon da aka ba wa wilayatul fakih (Jagorancin malami)?
    8874 گستره عمل ولی فقیه 2012/07/26
    Dalilan shugabancin malami (wilayatul fakih) suna bayyana cewar, fakihi shi ne wanda yake jagorantar al’umma ta musulmi, kuma yake maye gurbin imamai ma’asumai (amincin Allah ya tabbata a gare shi) a zamin da imami yafaku (boye). Ta wannan matashiyar wilayatul fakih (Shugabancin malami) tana da abubuwan da ...
  • Ya Ma’aunin Ubangiji ya ke wajen zabar wasu gungu daga cikin mutane domin ya ba su mukamin Annabta?
    6465 The Recognition of the Holy Prophet 2017/05/21
    Nufin Allah da iradar sa na da tsari da kaidoji (ko dokoki), kuma ayyukan sa ba mara sa ma’ana da manufa ba ne, ballantana ma bisa tsarin na hikima da ilimi da tausayi yake zaratar da komai. Don haka ne ma yake zabar wasu daidaiku daga ma’abota ...
  • Yaya asalin mutum yake?
    23895 خلقت انسان 2012/07/25
    Littattafan riwaya da na tarihi sun tabbatar cewa dan’adam wanda ke kan doron kasa bai kasance an same shi daga Habilu da Kabilu ba, shi dai an same shi daga dan Annabi Adam (amincin Allah ya tabbata a gare shi) na uku mai suna Shisu ko Hibatullah.
  • Me ye alaka tsakanin Zuhudu da ci gaban zamani?
    12295 Halayen Nazari 2012/07/24
    Kalmar zuhudu da saukin rayuwa suna daga kamalar halaye, wanda ya koma zuwa ga littattafanmu na shari'a zai samu cewa sun muhimmantar da wannan kalma da yawa, kuma sun karfafa ta sosai, suna masu nuni da kwadaitarwa da rashin damfaruwa da duniya da adonta, sai dai abin ...
  • me ye sharuddan jagorancin malami?
    8619 شرائط و خصوصیات ولی فقیه 2012/07/24
    Sharuddan asasi na jagoran musulunci sun hada da: ilimi, adalci, ikon tafiyar da al'ummar musulmi. Kuma a asalin doka ta dari da tara ta kundin tsarin dokar jamhuriyyar musulunci an yi nuni da wadannan sharuddan kamar haka: Sharudda da siffofin jagora: 1- siffantuwa ...

Mafi Dubawa