advanced Search
Dubawa
5300
Ranar Isar da Sako: 2015/05/18
Takaitacciyar Tambaya
Mene ne hukuncin sallar mamaci a fikihun Ja’afariyya? Kuma yaya ake yin ta?
SWALI
Mene ne hukuncin sallar mamaci a fikihun Ja’afariyya? Kuma yaya ake yin ta?
Amsa a Dunkule
Amsar malaman Shi'a game da wannan tambaya yana kamar haka ne:
1. Yin salla ga mamaci musulmi ko yaron da yake da hukuncin musulunci[1] da ya kai shekara shida, wajibi ce[2].
2. Sallar mamaci kabbarori biyar ce kuma akwai ambaton Allah tsakanin kowace kabbara da bayani hakan ya zo kamar haka:
Bayan niyya da fadin kabbara sai a ce: «اشْهَدُ انْ لٰا إِلٰهَ إِلَّا اللّٰهُ وَ انَّ مُحَمَّداً رَسُولُ اللّٰهِ صلى اللّٰه عليه و آله و سلم» wato; »Na shaida babu abin bauta sai Allah kuma hakika Muhammad manzon Allah (s.a.w) ne«.
Bayan kabbata ta biyu sai a ce: «اللّٰهُمَّ صَلِّ عَلىٰ مُحَمَّدٍ وَ آلِ مُحَمَّدٍ»  wato; »Aminci ya tabbata ga Muhammad da aalayen Muhammad«.
Bayan kabbara ta uku sai a ce: «اللّٰهُمَّ اغْفِرْ لِلْمُؤمِنينَ وَ الْمُؤمِناتِ» wato »Allah ka gafarta wa muminai maza da muminai mata «.
Bayan kabbara ta hudu idan mamacin namiji ne sai a ce: «اللّٰهُمَّ اغْفِرْ لِهٰذَا الْمَيِّتِ» wato; »Allah ka gafarta wa wannan mamaci«, idan kuma mace ce sai a ce: «اللّٰهُمَّ اغْفِرْ لِهٰذِهِ الْمَيِّتِ» wato; »»Allah ka gafarta wa wannan mamaciya«. Bayan kabbara ta biyar sai a fada, da an fade ta to salla ta kare ke nan.
Wannan abin da aka kawo ya isa a sallar mamaci. Sai dai yana da kyau a kawo ambaton Allah mai yawa fiye da haka, sai a yi ta kamar yadda zamu kawo a nan kasa:
Bayan kabbarar farko sai a ce:
«اشْهَدُ انْ لٰا إِلٰهَ إِلَّا اللّٰهُ وَحْدَهُ لٰا شَرِيكَ لَهُ وَ اشْهَدُ انَّ مُحَمَّداً عَبْدُهُ وَ رَسُولُهُ ارْسَلَهُ بِالْحَقِّ بَشيراً وَ نذِيراً بَيْنَ يَدَىِ السَّاعَةِ»
Wato; »Na shaida babu abin bauta sai Allah shi kadai ba shi da abokin tarayya gare shi, kuma na shaida cewa Muhammad bawansa ne kuma manzonsa ne da ya aiko shi da gaskiya yana mai albishir da gargadi game da tashin alkiyama «.
Bayan kabbata ta biyu:
 «اللّٰهُمَّ صَلِّ عَلىٰ مُحَمَّدٍ وَ آلِ مُحَمَّدٍ وَ بارِكْ عَلى مُحَمَّدٍ وَ آلِ مُحَمَّدٍ وَ ارْحَمْ مُحَمَّداً وَ آلَ مُحَمَّدٍ كَافْضَلِ ما صَلَّيْتَ وَ بٰارَكْتَ وَ تَرَحَّمْتَ عَلىٰ ابْراهِيمَ وَ آلِ إِبراهيمَ انَّكَ حَميدٌ مَجيدٌ وَ صَلِّ عَلىٰ جَميِع الأَنْبيٰاءِ وَ الْمُرسَلينَ وَ الشُّهَداءِ وَ الصِّدِّيقينَ وَ جَميِع عِبٰادِ اللّٰهِ الصّٰالِحينَ»
Wato; »Allah ka yi aminci ga Muhammad da aalayen Muhammad, ka yi albarka ga Muhammad da aalayen Muhammad ka yi rahama ga muhamma da aalayen Muhammad, fiye da yadda ka yi aminci kuma ka yi albarka kuma ka yi rahama ka Ibrahim da aalayen Ibrahim, hakika kai abin yabo ne da godewa, ka yi aminci ga dukkan annabawa da manzanni da shahidai da siddikai da dukkan bayin Allah na gari «.
Bayan kabbara ta Uku:
«اللّٰهُمَّ اغْفِرْ لِلْمُؤمِنينَ وَ الْمُؤمِنٰاتِ وَ الْمُسْلِمينَ وَ الْمُسلِمٰاتِ الْأَحْيٰاءِ مِنْهُمْ وَ الْأَمْوٰاتِ تابِعْ بَيْنَنٰا وَ بَيْنَهُمْ بِالخَيْراتِ انَّكَ مُجيبُ الدَّعَواتِ انَّكَ عَلىٰ كُلِّ شَيْ‌ءٍ قَدِيرٌ».
Wato; »Ubangiji ka gafarta wa muminai maza da muminai mata da musulmi maza da musulmi mata rayayyu daga cikinsu da matattu, ka kuma bi tsakaninmu da tsakaninsu da alherai domin kai ne mai amsa kira, kai mai iko ne a kan komai «.
Bayan kabbara ta hudu: Idan mamacin namiji ne sai a ce:
«اللّٰهُمَّ إِنَّ هَذٰا عَبْدُكَ وَ ابْنُ عَبْدِكَ وَ ابْنُ امَتِكَ نَزَلَ بِكَ وَ انْتَ خَيْرُ مَنْزولٍ بِهِ اللّٰهُمَّ إِنّا لٰا نَعْلَمُ مِنْهُ الّا خَيْراً وَ انْتَ اعْلَمُ بِهِ مِنّا اللّٰهُمَّ انْ كٰانَ مُحْسِناً فَزِدْ فِى احسٰانِهِ وَ انْ كٰان مُسِيئاً فَتَجٰاوَزْ عَنْهُ وَ اغْفِرْ لَهُ اللّٰهُمَّ اجْعَلْهُ عِنْدَكَ فى اعْلٰى عِلِّيّينَ وَ اخْلُفْ عَلىٰ اهْلِهِ فِى الْغابِرِينَ وَ ارْحَمْهُ بِرَحْمَتِكَ يا ارْحَمَ الرَّاحِمينَ»
Wato; »Ubangiji wannan dai bawanka ne dan bawanka, dan baiwarka, ya sauka gun ka, kuma kai ne mai fiyayyen masauki gare shi. Ubangiji mu ba mu san komai ba gare shi sai alheri, kuma kai ne ka fi mu sanin sa fiye da mu. Ubangiji idan ya kasance mai kyautatawa to ka kara masa cikin kyautatawarsa, kuma idan ya kasance mai munanawa to ka ketare masa ka yi masa afuwa ka gafarta masa. Ubangiji ka sanya shi gun ka daga cikin mafi daukakar masu daukaka, ka sanya wasu daga masu nagarta masu mayewa ga ahlinsa, ka yi masa rahama da rahamarka ya kai mafi tausayin masu tausayi «. Haka nan ma a fada bayan kabbara ta biyar, sai dai idan mamacin mace ce bayan kabbara ta hudu sai a ce:
«اللّٰهُمَّ إِنَّ هٰذِهِ امَتُكَ و ابْنَةُ عَبْدِكَ وَ ابْنَةُ امَتِكَ نَزَلَتْ بِكَ وَ انْتَ خَيْرُ مَنْزُولٍ بِهِ اللّٰهُمَّ انَّا لٰا نَعْلَمُ مِنهٰا الّٰا خَيْراً وَ انْتَ اعْلَمُ بِهَا مِنَّا اللّٰهُمَّ انْ كانَتْ مُحْسِنَةً فَزِدْ فِى احسٰانِهٰا و انْ كانَتْ مُسِيئةً فَتَجاوَزْ عَنْهٰا وَ اغْفِرْ لَهٰا اللّٰهُمَّ اجْعَلْهٰا عِنْدَكَ فِى اعْلىٰ عِلِّيِّينَ وَ اخْلُفْ عَلى اهْلِهٰا فى الْغٰابِرينَ وَ ارْحَمْهٰا بِرَحْمَتِكَ يا ارْحَمَ الرَّاحِمينَ».
»Ubangiji wannan dai baiwarka ce ‘yar bawanka, ‘yar baiwarka, ta sauka gun ka, kuma kai ne mai fiyayyen masauki gare tai. Ubangiji mu ba mu san komai ba gare ta sai alheri, kuma kai ne ka fi mu sanin ta fiye da mu. Ubangiji idan ta kasance mai kyautatawa to ka kara mata cikin kyautatawarta, kuma idan ta kasance mai munanawa to ka ketare mata ka yi mata afuwa ka gafarta mata. Ubangiji ka sanya ta gun ka daga cikin mafi daukakar masu daukaka, ka sanya wasu daga masu nagarta masu mayewa ga ahlinta, ka yi mata rahama da rahamarka ya kai mafi tausayin masu tausayi«[3].
 
 

[1].  Wato uba da uwar yaron ko daya daga cikinsu ya kasace musulmi ne.
[2]. Taudhihul masa’il (hashiyar Imam khomain), j 1, s 333, m 594.
[3]. Abin da ya rigaya, s 337, m 608.
TARJAMA YA JAWABU KATIKA LUGHA NYENGINE
Mahanga
Idadi ya maoni 0
Tafadhali ingiza thamani
Imel : Yourname@YourDomane.ext
Tafadhali ingiza thamani
Tafadhali ingiza thamani

MPANGILIO WA KIMAUDHUI

Tambayoyi Masu Fadowa

  • Me ye alaka tsakanin Zuhudu da ci gaban zamani?
    9967 Halayen Nazari 2012/07/24
    Kalmar zuhudu da saukin rayuwa suna daga kamalar halaye, wanda ya koma zuwa ga littattafanmu na shari'a zai samu cewa sun muhimmantar da wannan kalma da yawa, kuma sun karfafa ta sosai, suna masu nuni da kwadaitarwa da rashin damfaruwa da duniya da adonta, sai dai abin ...
  • idan mas'alar jagorancin malami tana ganin cewa kafa jagora ne, to me ye gudummuwar mutane a ciki?
    6405 انتصاب یا انتخاب 2012/07/24
    Duk da akwai nazarin cewa idan muna son mu sanya dokoki da bai kebanta da wani wuri ko zamani ba, ba mu da wata hanya sai zaben da mutane zasu yi. Kuma akwai hanyoyi biyu da suka shafi sharuddan zabar jagora kamar haka:
  • menene abin sha mai tsarkakewa?
    16553 شراب طهور 2012/09/16
    "Ashsharab" abin nufi duk abin sha "Addahiru" abin nufi mai tsaki mai tsarkakewa wannan kalma an yi amfani da ita a cikin ayoyi daban-daban a gidan aljanna ana samun abin sha mai tsarki mai dadi iri-iri mai yanayi kala-kala, hakika Kur'ani mai girma ya kawo maganar sa ...
  • Me ya sa ‘ya’yan imamu Husain suka girmi ‘ya’yan imamu Hasan (a.s)?
    5752 اهل بیت و یاران 2012/07/25
    Wannan ba wani abin mamaki ba ne, domin ba wata hujja ta al’ada da ta hankali da ta hana ‘ya’yan kani su girmi ‘ya’yan wa, mussam idan ya zamana tazara tsakanin yan’uwa biyun ba mai yawa ba ce kamar yadda ya kasnce tsakanin Hasan da Husain (a.s). ...
  • wanene mu”azu dan jabal?
    6923 برخی صحابیان 2016/07/12
    Mu”azu dan jabal dan amru dan ausu dan a”izu, ane masa alukunya da baban Abdurrahman, sannan ya na daga cikin mataimakan manzon Allah {s.a.w}.[1] mu”azu dan jabal tare da mutane 70 na daga cikin wadanda sukai mubaya”mar akaba sannan suka yi tarayya cikin yakoki ...
  • mene ne ma’anar Takawa?
    15032 تقوی 2012/07/25
    Takawa wani karfi ne cikin ruhin mutum mai tsawatarwa da hana shi aikata ayyukan kuskure, kamalar takawa na kasancewa in an hada da nesantar abubuwan haramun, kamar nesantar shubha. Kuma ita Takawa tana da marhaloli da rabe-rabe, da kuma alamomi, zamu bijiro da su a jawabi na ...
  • shin Allama Majlisi na daga cikin wadanda suka habaka Daular Safawiyawa, kana mai yaba wa mahukuntanta?
    5798 شخصیت های شیعی 2012/07/24
    Dangantaka tsakanin malaman Shi’a da mahukuntan daular Safawiya da ma mahukunta na wasu dauloli da nufin raunana Shari’a ba ne. Dalilan yin hakan su ne samar da mamora da kyakkyawan manufa ga al’umma da yin wannan alakar kan haifar don taimakon jama’a da yada Mazhabar Shi’a da ...
  • Shin da wacce mahanga Kur’ani ke kallon mutum? a matsayin wanda yake yin zalunci da jahilci, ko kuma halifan Allah a bayan kasa?
    10143 انسان و خلافت الاهی 2012/07/25
    1- Kur’ani ya yi nuni a wasu ayoyi cewa mutum na da matsayi madaukaki sai dai amma a wani bangaren da mafiya yawan ayoyi yana zarginsa da tare da yi masa gargadi 2-matsayin dan Adam dan Adam na da wani abin mai ban mamaki wajan ...
  • don me ake kiran annabi Muhammad (s.a.w) amintacce?
    4234 تاريخ بزرگان 2019/06/12
    Amintacce shi ne kishiyan mayaudari, watau ana nufin mutumin da ba ya yaudarar jama’a, kuma kowa ya natsu da shi ya dogara da shi bisa kyawun dabi’unsa. Idan muka waiga zuwa ga halayen Annabi (s.a.w) ta mu’amala da daidaku da al’umma tun a samartakarsa, zamu ga amana ...
  • ina so a ba ni tarihin Jundubu dan Janadata (Abuzarril Giffari)?
    15535 شخصیت های شیعی 2017/06/17
    Ya kai dan’uwa mai girma; Muna baka hakuri saboda jinkirin da aka samu wajen bada amsar tambayarka a sakamakon wasu larurori na aiki:- Shi ne jundubu dan janadata ko kuma a ce Abuzarril giffari yana daga cikin manyan sahabban manzo tun a farkon manzanci ya kasance ...

Mafi Dubawa