advanced Search
Dubawa
20762
Ranar Isar da Sako: 2007/10/04
Takaitacciyar Tambaya
Ta wace hanya za mu iya kare kanmu daga kanbun baka?
SWALI
Wace aya ce daga ayoyin Kur\'ani ke da tasiri wajen tsare kai daga maita da kambun baka.
Amsa a Dunkule
Kanbun baka na da tasiri a ruhin mutun wanda babu wani dalili da za a iya kore samuwar sa da shi, ballantana ma an ga faruwar abubuwa masu yawa da suka tabbatar da samuwar kanbun baka ko maita.
Marigayi shekh Abbas Kummi ya yi wasici da a riKa karanta aya ta 51 daga cikin surar Kalam mai albarka domin kare kai daga maita, kuma wannan ayar tare da la’akari da sha’anin saukarta ta dace da ayi amfani da wajen tsare kai daga kanbun baka.
Kari a kan wannan aya ruwayoyi sun yi takidi kan karanta wasu surori wanda daga cikinsu akwai suratun Nasi da FalaKi da Hamdu da Tauhid dss.. kuma da yawa daga cikin litattafan tafsiri sun karafafa hakan a yayin da suke yin sharhin waDannan ayoyi kan mihimmanzin karata wannan surori.
Amsa Dalla-dalla
HaKiKa kambun baka na da tasiri a ruhin mutum wanda hakan ya faru a zahiri ba sau Daya ba ba sau biyu ba sannan kuma babu wabi dalili kan kore samuwar sa kamar yadda aka samu ruwayoyi da suka dace kan ingancin wannan mas’ala. An cirato daga Manzo (s.a.w) a tafsirin durrul Mansur yana cewa : kanbun baka na shigar da mutun kabari kuma yana shigar da raKumi tukunya”[1].
Ya ce: Aliyu bn Ibrahim ya karBo daga Babansa shi ma ya karBo daga wajen wani mutuminmu, shi ma ya karBo daga Kaddah shi ma ya karBo daga Abu Abdullahi (a.s) ya ce: Amirul Muminina (a.s) ya ce: Annabi (s.a.w) ya yiwa Hasan da Husaini RuKiyya da wasu addu’o’in da suke rubuta su da killace su don tunkuDe sharrin kambon baka an ace musuTa’awizi sai ya ce: “Ina neman Allah ya kare ku albarjacin kalmomin Allah cikakku da sunayensa kyawawa daga sharrin dangi da Kwari da shaiDanu da mutane da sharrinduk wata idaniya mai cutarwa, haka ma sharrin maihassada idan ya yi hassada” sai Annabi (s.a.w) ya waiwayu wajenmu ya ce: Haka Ibrahim yake yiwa Isma’il da IshaK (a.s) ta’awizi([2]). Yazo a cikin hikima ta 400 a cikin Nahjul Balaga “kambun baka gaskiya ne ruKiyya ma gaskiya ce”([3]). Cikin waDan nan ruwayoyin ya bayyana cewa kambun baka ba zato bane ba Karya bane, kai abu ne tabbatacce, akwai shi, kuma akwai hanyoyin kawar dashi.
Cikin ayoyin da suka shahara na kare kai daga sharrin kambun baka akwai aya ta 51 a suratul Kalam mai albarka Allah Ta’ala ya cewa Annabinsa mai girma (s.a.w) a wannan ayar: “Lallai waDanda suka kafirta sun kusa sa ka faDi saboda kallon da suke maka a lokacin da sukaji karatun  Kur’ani sukadinga cewa lallai Muhammad Mahaukaci ne”([4]).
An yi Magana kan dalilin saukar ayar nan cewa:
Ance: “Banu Asad suna da kambun baka, don haka wani a cikinsu yakan Ki cin abinci har tsawon kwana uku in ya wuce ta kusa da wani sai ya ce: “Ban taBa ganin irinsa ba, nan take kambun baka ya kama shi, sai aka samo wani mai kambun baka don ya cutar da Annabi (s.a.w), sai ya ce: Banga wani mutum kamar kaba a yau, nan take Allah yak are Manzon Allah (s.a.w).[5]
Allama DabaDaba’i (ra) ya yi bayani kan wannan ayar yake cewa: A ra’ayoyin gaba Dayan malaman Tafsiri sunce: “IzlaKbil absar a yar” LayuzliKuna ka” shi ne kambunbaka, wanda shi kambun baka tasiri ne wanda ke cikin nafsu, bamuda dalilin kore haka, kai abubuwan da suka faru masu yawa sun nuna ingancin ma’anar kambun baka.
Don haka ba dalilin da zai jawo muyi musun kambun baka, ballantana muce aKidar Karya ce([6]).
Akan haka ne sheikh makarim shirazi yake cewa:
Shin tasirin kambun baka gaskiya ne?
Mutane da yawa sun Kudirce cewa kambun baka nada tasiri musamman lokacin  da ka kalli abu ya burgeka, saboda sauda yawa hakan yakan jawo abu ya karye ko ya lalace, idan abin da aka kalla mutum ne tofa zai iya yin rashin lafiya koya haukace.
Tabbas wannan mas’alar ba mustahiliya bace a hankalce, saboda wasu malaman zamanin nan sunce akwai Karfin maganaDisu na musamman wanda ke Boye a cikin idanuwa, zai yiwu ya yi aiki da yawa, kamar yadda zai yiwu a jarraba hakan da kuma Karfafa hakan. Sannan abu ne cewa “sa bacci ta hanyar maganaDisu dake cikin idanuwa.
Tabbas tartsatsin hasken haske ne wanda yake iya yin aikin da ba wani mugun makamin da zai iya yinsa, don haka dole akwai wani Karfi a cikin wasu idanuwa da yake da tasirin a kan waDanda suka kalla, hakan kuwa sanadiyyar wasu tsirkiyoyi ne na musamman (Special waBes) wannan ba wani baKon abu bane.
Mutane da yawa sun faDa cewa sunga wasu mutane da idonsu sunjawo halakar wasu (mutane da dabbobi dama wasu abubuwa) saboda ganinsu ya cutar dasu([7]).
Zamahshari ya naKalto daga Hasanul Basari (Babban malamin ‘yan sunna) cewa karanta wannan ayar na tunkuDe tasirin kambun baka([8]).
Haka ma sheikh Abbasul Kummi Babban malamin Hadisi wanda ya wallafa mafatihul Jinan ya faDa a wannan littafin – cikin bayanin wasu addu’o’in tsarin kambun baka cewa ayar “Wa in ya kadul lazzina kafaru” karanta ta ne maganin kambun baka([9]).
Tabas daga cikin ruwayoyin da wasu daga cikin tafsirai mabanbanta suka faDi kan wannan ayar ba su kawo ruwayoyin da ke nuna cewa tana magance maita ba. [10]
Babban malamin Hadisi Allama Majalisi (ra) a bayanin tunkuDe sharrin kambun baka – bayanya yi bayanin ruwayar Durrul Mansur da muka faDa Dazu – akwai ruwayar Imam SadiK (a.s) don tunkuDe tasirin kambun baka yake cewa a ciki mutum ya karanta “Masha Allah La Kuwata illa billlahil Aliyul Azim”, ko ka karanta Kul’a uzu bi rabbin nas da Kul’a uzu bi rabbinl falaK, a wata ruwayar ya ce ka karanta fatiha da Kulhuwalllahu. Amma a lokacin day a faDi wannan addu’o’in bai kawo waccan ayar ba([11]).
Abisa wannan maganar, tabbas tasirin kambun baka sannanen abu ne, akwai wasu addu’o’in da suke tunkuDe tasirin kambun baka.
Don Karin bayani ka duba Tafsiril Amsal J.24 sh 426.
 

[1] Durrul Mansur fi tafsiril ma’asur j 6 shafi na 258.
[2]Kafi J.2 sh 569 Hadisi na 3. An karBo daga Ali Dan Ibrahim daga shashin sahabbansa daga Kaddah daga babansa Abdullah (a.s) ya ce: shuganaban muminai (a.s) ya ce: Manzo (s.a.w) ya yi wa Hasan da Husain tofi (ruKiyya) sai ya ce ina nema muku tsari da Kalmar Allah cikakkiya da sunayensa kyawawa dukkaninsu baki Daya daga sharrin mai safi mai cutarwa da kuma dukkanin wata idaniya mai aibi da sharrin mai hasada idan ya yi hasada, sannan sai ya juwo wajen mu ya ce haka Annabi Ibrahim (a.s) ya kasance yana yiwa ismail da ishaK (a.s).
[3] Nahjul Balagah sh  547. (maita gaskiya ce kuma tofi ma gaskiya ne)
[4] surat kalam 51{ya kusata waDannan da suka kafirta kambun bakasu ko maitar su ta kama ka a lokacin da suka ji tunatarwa suna cewa lalle wannan mahaukaci ne alhali ba komai ba ne (kake isarwa) face tunatarwa ga talikai} tafsirul mizan, allama taba’taba’I, j 19 shafi na 636.
[5]Alkashif na zamashakari, J.3 dana 4, sh 1278, bugun darul ahya’i.
[6] Almizan J. 19 sh 648.
[7] Al amsal Fi Tafsirl kitabillahil munzal J.18 sh 562.
[8] Alkashif J.3dana 4, sh 1279.
[9] Mafatihul jinan sh 319, Abbaskuhmmi bai fada a safinatul Bihar  karanta wannan ayar na tunkude kambun baka ba.
[10] Tafsirul mizan J.19, sh 651, Tafsirin Nasim Rahamat sh 71, Tafsirin Nurl sakalain J.5 sh 400, Tafsirul Amsal J.24, sh 426.
[11] Hilyatul muttaKin na allama majlisi shafi 319, maDaba’ar hijra.
TARJAMA YA JAWABU KATIKA LUGHA NYENGINE
Mahanga
Idadi ya maoni 0
Tafadhali ingiza thamani
Imel : Yourname@YourDomane.ext
Tafadhali ingiza thamani
Tafadhali ingiza thamani

Tambayoyi Masu Fadowa

Mafi Dubawa