advanced Search
Dubawa
3594
Ranar Isar da Sako: 2012/04/03
Takaitacciyar Tambaya
An samu ruwaya ginanniya kan cewa Allah (s.w.t) ya haramtawa yayan Fatima shiga wuta, ina rokon a warware min wannan Magana
SWALI
Ina rokon a bayyana min matsayin wannan hadisi ta fuskacin dangane daga Manzo (s.a.w) cewa: “hakika Fatima ta kiyaye farjinta sai Allah (s.w.t) ya haramtawa ya’yanta (zuriyarta) shiga wuta” bihar bolume 43 page 20, 23, 232
Amsa a Dunkule
Wannan ruwaya an rawaitota daga litattafan Shi’a da na sunna, ana kuma ganinta daga ingantattu sabida yawan rawaitatta da aka yi da kuma litattafan da tazo daga ciki, saidai yadda ake ganin yanayin da tazo da shi na farko wajan game sukkan yayan Fatima a ciki, zamu iya fahimta daga wata ruwaya cewar ya’yan Fatima da aka yi wa wannan busharar su ne wadanda suka kame kansu daga zunubi, sabo da tsarkinsu da kamewarsu, ko kuma saboda kamewarta suka zamo amana daga shiga jahannama, ko kuma wanzuwarsu cewa su zuriyarta ne ya zama suna da iyakar da ta kare musu azaba, idan sun kasance tasgatattu ne na daban.
Amsa Dalla-dalla
An samu ruwaya cikin bihar da wannan yanayin da cikckken dangane daga imam ridha (a.s) daga iyayensa ya ce: Manzo (s.a.w) ya ce: “Hakika Fatima ta kiyaye farjinta sai Allah (s.w.t) ya haramtawa ya’yanta (zuriyarta) shiga wuta”[1]. Haka wannan ruwaya akwaita cikin littafi uyun akhbarur Ridha (a.s) wanda yake a Bihar da wannan lafazi[2].
Hakanan wannan ruwaya an fadeta cikin litattafai da dama, hakanan daga marawaita hadisi daga Shi’a da sunna, kuma anyi duba tare da tambayoyi da yawa a kanta[3]. wanda wannan ma ke iya nuni zuwa ingancinta tare da sallama mata. Wasu daga mawallafan sunna a karni na goma bayan karatunsa game da ruwaya ya isa zuwa natijar ingancinsa da ya ciro daga wannan ruwaya cewa danganensa ingantacce ne, ita ba wai na daga duban da wasu ke yi bane, kamar yadda wasu suka bayyana a wasu litattafan[4], amma abin da ya cancanci bincike da tattaunawa cikin wannan ruwaya shi ne fadin maganarsa da gamewarsa. Shin ka samu ayyanannen daya na zuriyarsa ko ta hada da dukkansu? Amma abin da muka iya fitrwa daga ruwayar Shi’a kamar na nuni cewa wasu daga shuwagabanni na ganin ingancinsa da hasken da ya samu daga Allah (s.w.t) tare da sauwwara asasin wannan hadisi cewa an gafarta musu duk zunubansu ne, kuma bazai kaisu zuwaga azaba ba!!, amma imamai ma’asumai (a.s) sun tsaya kan wannan istinbadi da tsanani suka sanar cewa misalin wannan ruwaya dole kada ayi mummunan aiki da ita ta bangaren masu zargi ga Ahlul-bait (a.s) kuma sukayi nuni zuwa wasu daga wadannan ruwayoyi:
  1. Daga Hassan dan musa ya ce na kasance a khurasan tare da imam Ali ridha (a.s) a wajan zama (majlisi) tare da Zaid dan musa (dan uwan imam riza wanda aka fi sani da Zaidun nar) zaidu dan Musa ya fuskanci wasu mutane a mazaunin yana yi musu alfahari yana magana, a lokacin abul Hassan na magana ga wasu mutane, sai imam yaji maganar zaidu ya juyo ga zaidu ya ce dashi: ya zaid baka samu maganar da mutanen kufa suka rawaito ba cewa: Fatima (a.s) ta kiyaye farjinta sai Allah (s.w.t) ya haramtawa zuruyrta shiga wuta! Ba kan kowa take ba sai kan Hassan, Husain, da dan cikinta kawai, koda imam Musa (a.s) ya bi Allah (s.w.t) ya azumci rana, ya tsaya cikin dare, kai ka saba masa sannan kuzo ranar alkiyama daidai, ko kuma ma kafishi wajan Allah (s.w.t)? Hakika imam ya fadi wannan ne game da wadanda sukayi aiki na gari daga cikinmu[5]. An samu daga wasu ruwayoyi masu kama da wannan ruwaya[6].
  2. Daga hammadu dan Usman ya ce nace da abi Abdullah (a.s): raina fansa gareka mene ma’anar fadin Manzo (s.a.w) cewa “hakika Fatima (SA) ta kiyaye farjinta sai Allah (s.w.t) ya haramta wuta ga zuriyarta (ya’yanta)”? Sai Imam ya ce: ‘yantattu daga wuta su ne dan cikinta, Hassan da Husain (a.s), zainab da ummu kulthum (SA)[7].
  3. Wani mutum ya ce da Imam Ja’afar (a.s) kuna ganin fadin Manzo (s.a.w) cewa: “Hakika Fatima ta kiyaye farjinta sai Allah (s.w.t) ya haramtawa ya’yanta (zuriyarta) shiga wuta”. Shin wannan ba zai zama amana ga dukkan ya’yan Fatima a duniya ba kuwa? Sai Imam Ja’afar ya ce: kayi wauta, ana nufin Hassan da Husain (a.s) ne kawai domin su ne tushen Ahlul-bait (a.s), duk wanda ba su ba idan yaki yin aiki nasabarsa da Fatima (a.s) bazata kaishi ba[8].
na’am akwai wasu ra’ayoyi da zamu iya fahimtar wanin wadancen ukun da muka ambata[9]. Sai dai ba zamu iya karbaba domin ta sabawa usul da tsarin musulunci da kurani, domi ma’anarta shi ne yanci kai tsaye wajan zuwa da mummuna da kariya daga azaba, duk da cewa munyi imani an kebace wasunsu, sai dai wannan saki baiyi daidai da koyarwar addini ba, amma tsarin yayan Zahra (SA) na nufi tazgacewar da Allah (s.w.t) ya yi mata sakamakon kamewar babarsu Zahra (SA), suma suka kame kansu domin koyi da ita daga dukkan zunubi da sabo tare da zabinsu kan hakan (yin aikin alkhairi ko na sharri).
 

[1] Majlisy, Muhammad albakir, bihar bolume 43, page 20, mu’assasatul wafa’a Beirut 1404;
[2] Sheikhus saduuk uyun akhbarur ridha (a.s) bolume 2, page 63,nashr jihan, Dhahran, 1378;
[3] Ibn shahr aashuub, munakibu aali abi dalib, bolume 3 page 325, nashrul aammah; Kum, 1379;
[4] Assalihy, ashshamy, subulul huda war rushd fi sirstu khairul ibad, bolume 11 page 250, darul kutubul ilmiyya Beirut, 1414
[5] Sheikhus saduuk, uyun akhbarur ridha (a.s) bolume 2, page 232, bolume 1;
[6] Al irbily, Aliyyu dan Musa, kashful gumma, bolume bolume 2, page 310, maktabatu bany hashimy Tariz, 1381;
[7] Sheikhus saduuk, muanil akhbar, page 106nashru jama’atul madrasatain Kum, 1361,.
[8] Ibn abil hadeed, sharhi nahjul balagah, bolume 18 page 252, maktabatu ayatullahil mar’ashy, Kum 1404.
[9] Arrawandy, kutbuddeen, alkhara’ij wal jara ih, bolume 1 page 281, mu’assasatul imamul mahdy (AF), Kum, 1409
TARJAMA YA JAWABU KATIKA LUGHA NYENGINE
Mahanga
Idadi ya maoni 0
Tafadhali ingiza thamani
Imel : Yourname@YourDomane.ext
Tafadhali ingiza thamani
Tafadhali ingiza thamani

MPANGILIO WA KIMAUDHUI

Tambayoyi Masu Fadowa

  • Ta wace hanya za mu iya kare kanmu daga kanbun baka?
    17285 Halayen Aiki 2017/05/20
    Kanbun baka na da tasiri a ruhin mutun wanda babu wani dalili da za a iya kore samuwar sa da shi, ballantana ma an ga faruwar abubuwa masu yawa da suka tabbatar da samuwar kanbun baka ko maita. Marigayi shekh Abbas Kummi ya yi wasici da a ...
  • me ya sa Kur’ani bai ba da izini ga mutanen da ba su da ikon yin aure dawwamamme su yi auren mutu\'a ba?
    4068 Tafsiri 2019/06/12
    Ayoyin Kur’ani dole ne mu hada su da juna domin mu samu fasara mai ma'ana: saboda wasu ayoyin na fasara wasu ne. a cikin wannan ayar nuni da cewa dukkan wadanda ba su da ikon aure dawwamamme ne ko mutu'a da su kame kansu, ba ya na ...
  • Ta wace Hanya ake mangance maita da kanbun baka?
    26391 Halayen Aiki 2017/05/21
    Lalle Alkura'ani ma ya tabbatar da akwai maita, inda ya nuna wasu alamu da suke gaskata abin da tarihi ya tabbatar na daga cikin abin da Al’kur'anin ya zo da shi na daga al’umman da suka shude. Wasu malamai a wannan zamanin suna ganin wasu daga cikin ...
  • mece ce mahangar musulunci a kan samuwar halittu masu rai a sauran duniyoyi?
    9277 آسمان و زمین 2012/07/24
    Akwai tunanin cewa a cikin sauran duniyoyi shin za a samu halittu masu rai ko hankali, daya daga cikin tambayoyin da dan Adam ke neman bayanin su, amma har yanzu bai samu ba. Wasu bayanai a Kur’ani na nuni da samuwar wasu halittu masu rai a duniyar ...
  • Me ake nufi da hukunci da fatawa? Me ye bambancinsu?
    9313 بیشتر بدانیم 2012/07/24
    Fatawa: Ita ce fitar da hukuncin wani lamari a addini ta hanyar koma wa madogarar shari’a da amfanuwa da garesu, ta hanyar da aka san ana fitar da hukuncin. Hukunci: Shi ne abin da ake zartarwa ta hannun jagoran hukumar musulunci. Jagora zai iya amfana ...
  • Tarihin Adam (as)
    16020 2019/06/16
    Amsa Filla-Filla: bayani kan rayuwar wasu nau”in mutane da aka fara halitta a bayan kasa, da kuma sanin shekara nawa kenan da halittar su zuwa wannan zamani da muke ciki? To hakika babu wata aya da ta yi bayanin hakan cikin kur”ani. Allama daba”ba”i cikin tafsirinsa na ...
  • shin Imamul hujja a tsibirin bamuda yake zaune?
    13801 کیفیت زندگی امام غایب 2012/07/25
    Dalilin da ya sa wasu mutane suka yi ammanar cewa “Tsibirin Bamuda shi ne mazaunar Imamu Mahdi (a.s), gani suke Tsibirin Bamuda shi ne “Jazijrayul Khadra’a”. Bisa kaddara cewa Jaziratuk Khadra’a ita ce mazaunar Imamu Mahdi (a.s) shi ya sa suka ce Tsibirin Bamuda ya kunshi wadannan ...
  • Me ake nufi da gaskiya, kuma wace hanya ce zata kai ga samun hakikanin gaskiya?
    19748 Sabon Kalam 2012/07/24
    Gaskiya tana nufin hanya matsakaiciya, wato ana nufin maganar daidai da bin hakika, gaskiya ita ce sanya komai da hikima bisa mahallinsa da ya dace da shi. Sannan bin gaskiya da tafiya kanta bisa tafarkinta a fagen tunani yana nufin tanadin makamin ilmi da mantik ...
  • Shin hukuncin da namiji ajnabi yake da shi game da mata, shi ne hukuncin Allah game da su, ta yadda zai zama dole sai sun rufe jikinsu yayin yin salla?
    8529 زن 2012/07/24
    Babu wani kokwanton cewa Allah (s.w.t) ya san komai, kuma a kowane hali, kuma babu wata ma’ana ga boye wa Allah wani abu, haka nan Allah (s.w.t) ba shi da hukuncin namiji ajnabi game da mace yayin addu’a? sai dai yayin ibada mutum yana samun kansa a ...
  • Me ake nufi da Koma wa malami, da koyi?
    8294 بیشتر بدانیم 2012/07/24
    Marja’anci da ma’anar kasancewar malami makoma ne shi a karbar fatawa wurinsa a fikihu yana kishiyantar ma’anar koyi da malami ne. Domin a ma’anar koyi yana nufin wanda bai kware ba kan wani lamari ya koma wa wanda ya kware, wato yana nufin ke nan a koma ...

Mafi Dubawa