advanced Search
Dubawa
8524
Ranar Isar da Sako: 2012/05/19
Takaitacciyar Tambaya
Me ya sa batun isma da biyayya ga imamai (a.s) da masu da’a bai samu gurbi ba kuma ba a tattauna batun ba zamanin imam Ali (a.s) da imam Hasan (a.s) kamar yadda aka yi a zamanin imam Sadik (a.s)?
SWALI
Me ya sa batun isma da biyayya ga imamai (a.s) da masu da’a bai samu gurbi ba kuma ba a tattauna batun ba zamanin imam Ali (a.s) da imam Hasan (a.s) kamar yadda aka yi a zamanin imam Sadik (a.s)?
Amsa a Dunkule

Zancen isma da biyayya ga Imamai Ma’asumai (a.s) an tattauna a kansu tun zamanin Manzon Allah (s.a.w). Sai da zamanin Imamu Sadik (a.s) ya bambanta da sauran zamuna nan sauran Imamai (a.s). Damar da ya samu ta fuskar zamatakewa da wayewa babu wani Imami (a.s) da ya samu wannan damar. Dalili kuwa shi ne, a lokaci da gwamnatin Banu Umayya ta raunana take tangal-tangal da karfafuwar ikon Abbasiyawa. Wadannan sassa biyun sun yi ta fafatawa lokaci mai tsawo a tsakaninsu. A gefe guda a zamanin Imamu Sadik (a.s) dama ta samu saboda hali da mulkin ke ciki sai ya zamana lokaci ne na farfadowar Musulunci da bunkasar ilimi.

Amsa Dalla-dalla

Zamu yi bahasi a batun isma da biyayya ga Imami ma’asumai (a.s) ta fuska biyu:

Na fako: Batun isma a zantukan Imamai (a.s):

Idan muka bi diddigi muka binciki nassosi da ke batu game da ismar Imamai (a.s) da yi musu biyayya, zamu ga akwai shi tun a farko-farkon zamanin manzanci a lokacin Manson Allah (s.a.w).

  1. Shafi’i ya ruwaito a littafin Manakib da isnadi zuwa ga Abdullahi bin Mas’ud ya ce: “Manzon Allah (s.a.w) ya ce: “Ni ne addu’ar Annabi Ibrahim (a.s).” Sai muka ce: “Ta kaka ka zama addu’ar babanka Annabi Ibrahim (a.s)? Ya ce: “Allah Ya yi wasici ga Annabi Ibrahim (a.s) “(ka ambata) zamanin da Ubangijin Ibramu Ya jarrabe shi da kalmomi ya ba da su cikakku Ubangiji Ya ce: “Hakika zan sanya ka abin koyi” Annabi ya ce: “Kuma ka sanya shugabannin nan daga cikin ‘ya’yana,” Ubangiji Ya ce: “Alkawarina na Shubanci ba ya samun azzalumai”.[1] Sai Annabi Ibrahim ya yi farinciki, ya ce: “Ya Ubangiji a zuriyata ma da akwai shugabanni irina? Sai Allah (SWT) Ya masa wahayi Ya ce: “Ya Ibrahim ba zan maka alkawari da ba zan cika maka ba. Ya ce: “Ya Ubangiji wane alkawari ne ba zaka cika mum shi ba”? Ya ce: “A cikin zuriyarka ba zan ba wa azzalumi shugabanci ba. A sannan sai Annabi Ibrahim ya ce: “Wane ne azzalumi a cikin zuriyata? Sai Ya ce masa: “Duk wanda ya yi sujjada ga gunki ya bauta musu ba Ni ba.” A sannan Annabi Ibrahim ya ce: “Ka nisanta ni da ‘ya’yana daga burin bautar gumaka, hakika sun badda mafi yawan mutane’.[2] Sai Annabi (s.a.w) ya ce: “Sai addu’ar ta iso gare ni ta iso ga Ali, a cikimmu babu wanda ya taba sujjada ga gunki, sai Ya zabe ni Annabi Ya zabi Ali wasiyyi”.[3]
  2. Kasim bin Kayis daya daga cikin sahabban Amirul muminina Ali (a.s) da Imamu Sajjad (a.s) na musamman ya ce: “ Ita da’a a kan yi ta ne ga Allah Shi kadai da ManzonSa da majibinta al’amarin da Allah Ya kusanta su a gare Shi da kanSa, inda Ya ce: “Ku bi Allah ku bi Manzo da ma’abuta al’amri daga cikinku. Allah Ya yi umurin da bin ManzonSa ne saboda ma’asumi ne tsarkakke kuma ba ya yin umurni a yi sabo, kuma Allah Ya yi umurni da bin ma’abuta lamari saboda su ma ba sa yin sabo kana ba sa umurni da a yi sabon Allah”.[4]
  3. A Nahjul balaga Amirul muminina (a.s) ya yi iShara game da batun isma:

A huduba ta 147 yana cewa: “Ba sa saban wa Addini, ba sa sabani da shi”.[5] Ba zai yiwu wani ya rasa sanin wani hukunci na Addini ba, balle ya samu sabani da masanin).

b. A huduba ta 131yana cewa bayan kore wasu sifofi ga buran Imamu Ali (a.s) ya ce: (s.a.w) “Ba mai watsi da hadisai ba ne, al’umma su halaka”.[6] A bisa dabi’a wannan na tabbatar da wajabcin biyayya ga Imami (a.s).

c. A huduba ta 105 yana cewa: Yaku mutane ku nemi haske da makamashin fitilar mai wa’azi da ya wa’zantu, ku kwankwada daga tataccen marmaro da ba ya gurbata.”[7]

Hakika an yi zantuka da dama da suka Shafi batun ma’asumai (a.s) a ruwayoyi a gurare daban-daban, amma zamu takaita a nan.

Na biyu: Dangane da dalilan da suka sanya yawan tattauna zancen akida a zamanin Imamai biyu watau Bakir da Sadik (a.s) fiye da a zamunan sauran Imamai (a.s) zamu bayyana a takaice. A bangaren siyasa, lokacin Imamu Bakir (a.s) musamman ma a lokaci Imamu Sadik (a.s) lokaci ne da gwamnatin Ummayawa ta raunana tana tangal-tangal, kana Abbasiyawa suka kara samun damar fada a ji. Kasantuwa lokaci ne da Umayyawa ke cikn tsaka-mai-wuya na siyasa ba su da wata dama ta tursasawa Imaman Shi’a (a.s) da cutar da su (irin lokacin Imamu Sajjad (a.s).

Sannan su Abbasiyawa sun daga tutar su ne da sunan kare Ahlin Annabi (s.a.w), da dauko fansar jininsu, kafin su hau kan mulki. A bisa kaskiya sun hau halifanci ne da wannan taken. Wannan shi ya sa babu wani tarihi da ya nuna an tursasa musu (a.s) a bangarensu a wanna lokacin. Wannan lokaci kyakkyawar dama ce ta yada ilimi da karantarwar Imamai (a.s). Kana daga cikin abubuwa da suka yi matukar tasiri a wannan batu (na akida) Sharuda na karantarwa na musamman da tattaunawa da sauran kunkiyoyi da mazhabobi na musulunci.[8]

 


[1] Bakara: 124.

[2] Ibrahim: 35-36.

[3] Sayyid Dawus, Aliyu bin Musa, a liffafin Dawa’if j1, sg78, daba’in Alkhiya’am.,Kum, 1400,HK.

[4] Salim bin Kayis Abusadik, a littafin Salim bin Kayis.sh884,, dabaa’in IntiShara’at Alhadi, Kum, 1415 HK.

[5] Nahajulbalaga zance na j1, sh 206 dabaa’in Darulhijra, Kum,

[6] A littafin da ya gabata sh153.

[7] A littafin da ya gabata 153.

[8] don karin bayani sai a dubi R.K: Imamu Mahdi, Siratul’a’imma, sh353, Mu’assasar Imamu Sadik (a.s) Kum,1415 HK.

 

TARJAMA YA JAWABU KATIKA LUGHA NYENGINE
Mahanga
Idadi ya maoni 0
Tafadhali ingiza thamani
Imel : Yourname@YourDomane.ext
Tafadhali ingiza thamani
Tafadhali ingiza thamani

MPANGILIO WA KIMAUDHUI

Tambayoyi Masu Fadowa

  • Shin jagorancin malami sakakke ba kuwa yana nufin a yi gaban kansa a hukuma ba ne?
    6911 گستره عمل ولی فقیه 2012/07/24
    Jagorancin malami wani isdilahi ne na fikihu da yake nuni da fagagen aiki da jagoranci da kuma wadanda suke karkashin wannan jagora, kuma babu wata iyaka a wannan fagen. Sai dai wannan ba yana nufin cewa babu kowace irin iyaka ko wasu ka'idoji a aiwatar da jagoranci ...
  • Shin ruwan maziyyi, waziyyi da wadiyyi najasa ne?
    11667 Hakoki da Hukuncin Shari'a 2020/05/19
    ruwan da yake fita daga jikin dan adam idan aka cire Bawali da Maniyyi ya kasu kamar haka:Na daya: Ruwan da yake fitowa bayan bawali kuma yana da danko kadan wanda ana kiransa Madiyyi.Na biyu: Ruwan da yake fita yayin jjin ...
  • a mahangar Kur’ani mene ne bambanci ibilis da shaidan?
    13579 ابلیس و شیطان 2012/07/24
    A bisa ayoyin kuráni mai girma ibilis yana daya daga cikin aljanu, saboda yawan ibadar shi ya zamo daga cikin mala'iku, amma bayan Allah ya halicci Adam sai aka umarce shi da yi wa Adam sujada amma ya ki sai Allah ya nisantar dashi daga gare shi. ...
  • Menene hukunchi namijin da ba ya iya biyawa matarsa hakkokinta?
    14408 2019/06/16
    dawwamar rayuwar aure da karfafarta ya dogara da soyayya da kauna da fuskantar juna da girmama juna. Domin iyali su samu tsayuwa da dawwama Addini Muslunci ya sanya hakkoki ga kowanne dayansu ya kuma ayyana musu wajibai a kansu, duk sa”ilin da aka ce akwai hakkoki to ...
  • WADAN NE BAITOCI NE ABBAS YAKE RERAWA A LOKACIN DA YA ZO DIBAN RUWA?
    11791 اهل بیت و یاران 2012/07/26
    Mayaka yayin mubaraza a zamanin da su kan yi amfani da wani zaurance (don shaida juna ko ba da sako a tsakaninsu) don haka su kan rera baitotocin waka don samar da karfin gwiwa ga mutanensu da raunana abokan gaba. Imam (a.s) da mutanensa sun yi amfani ...
  • Me ake nufi da hukunci da fatawa? Me ye bambancinsu?
    11751 بیشتر بدانیم 2012/07/24
    Fatawa: Ita ce fitar da hukuncin wani lamari a addini ta hanyar koma wa madogarar shari’a da amfanuwa da garesu, ta hanyar da aka san ana fitar da hukuncin. Hukunci: Shi ne abin da ake zartarwa ta hannun jagoran hukumar musulunci. Jagora zai iya amfana ...
  • Me ye mafi dadewar madogarar jagorancin malami da ake da ita?
    7668 پیشینه تاریخی ولایت فقیه 2012/07/24
    Mafi dadewar madogara game da wilaya ko jagoaranicn malami da muke da ita sun hada da littafin Mukni'a na sheikh mufid ne, ya kawo wannan bahasi a babin umarni da kyakkyawa da hani ga mummuna a matsayin daya daga cikin abubuwan da suka hau kan malami.
  • shin ahalissunna sun canzama ayoyin gadir da zuka zo a cikin kur'ani wuri?
    15170 غدیر خم 2012/11/21
    Mafiya yawa na masu fassarar kur'ani daga bangaren sunna da shi'a, sun tafi akan cewa; اليوم يئس الذين jimlace wadda tazo tsakanin aya ta ukku ta suratul ma'ida dan haka acin ilimin nahawu bata da muhalli na li'irabi. Kuma mafiwa yawancin su suna ganin wannan ta'aruz ...
  • A kawo hadisan da suka yi haramta rawa da kuma madogararsu.
    16064 بیشتر بدانیم 2013/08/15
    Kafin mu ba da amsar wannan tambayar ya kamata mu lura da wani abu guda mai muhimmanci kamar haka, dan an samu ruwaya daya a cikin litattafan ruwayoyi bai wadata ba wajan kafa dalili da ita ruwayar. Domin kafa dalili da ruwaya wani abu ne da ya ...
  • Menene gaskiyar maganar da ke cewa “Duk wani maniyyin da aka kyan kyashe cikin daren babbar salla dan zai zamto mai yatsu shida ko hudu”?
    24767 Dirayar Hadisi 2012/07/26
    Manzo (s.a.w) ya fada cikin mustahabbai da makaruhan jima’i cikin hadisi mai tsayi, ga Imam Ali (a.s) cewa: “ … ya Ali ka da ka tara da iyalinka cikin daren babbar salla domin idan Allah yai nufinku da samun da a wannan dare zai zamo mai yatsu ...

Mafi Dubawa